Asalin hoton, EFCC
Hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa ta Najeriya EFCC ta ce an kai wa jami'anta masu sa ido kan amfani da kuɗi a wajen zaɓe hari a Abuja da Imo.
Hukumar ta ce wasu 'yan daba ne suka kai wa jami'an nata hari a kusa da fadar sarkin Bwari da ke Abuja, babban birnin ƙasar.
Wata sanarwa da EFCC ɗin ta wallafa a shafinta na twitter ta ce, harin ya biyo bayan kame wani mutum da hukumar ta yi, wanda ya ke tsara siyen ƙuri'a a yankin na Bwari.
Sanarwar ta ce tuni hukumar ta kama mutumin mai kimanin shekara 30, sannan ta ƙwace jerin sunayen wasu mutane da ya riga ya tura musu kuɗi asusunsu na banki.
Wannan labari ne na dauke da bayanai da X suka bayar. Muna neman amincewarku kafin mu dora muka, saboda nuna iya dauke da wasu bayanai da aka iya adanawa. Watakila kana za ka so ka karanta X da tsarin bayanan da za a adana da da tsarin sirri kafin ka amince. Idan kana son ganin wannan bayani ka zabi ‘amince sannan ka ci gaba’.
Karshen labarin da aka sa a X
Babu karin bayanai
A lokacin ne fusatattun matasan suka yi kukan kura suka yi kan jami'an na EFCC inda suka farfasa gilasan motocin hukumar.
Hukumar ta ce sun samu nasarar tarwatsa matasan ne bayan da jami'anta suka yi harbi sama, don gargaɗin 'yan daban.
A jihar Imo ma, hukumar ta ce an kai wa jami'anta hari da bindiga, inda aka harbe su daga wasu motoci biyu a mazaɓar makarantar firamare ta Mann.
EFCC ta ce maharan sun gudu ala tilas, bayan da jami'an hukumar suka mayar da martani.
Hukumar dai na zargin cewa maharan masu siyen ƙuri'a ne.
© 2025 BBC. BBC ba za ta dauki alhakin abubuwan da wasu shafukan daban suka wallafa ba. Karanta hanyoyin da muke bi dangane da adireshin waje.
An kai wa jami'an EFCC hari a Abuja da Imo – BBC
