Asalin hoton, Getty Images
Wannan tambaya ce da mazauna babban birnin kasar ke ta faman yi a kullum a 'yan watannin nan, tun bayan yawaitar hare-haren 'yan bindiga masu satar jama'a a birnin da kewaye.
Abubakar Isa, wani dan asalin jihar Kano kuma mazaunin Abuja ya shaida wa BBC yadda yake zaman dar-dar a babban birnin.
"Inna lillahi Wa Inna Ilaihirrajiun! Yanzu Abuja babu inda yake da tsaro. Mu kanmu da muke a Gwarinpa muna cikin zulumi.
Yanzu zan daina bin hanyar Bwari idan zan je Kano. Gwara kawai na bi ta Zuba duk da acewa akwai bambancin tazarar kilomita kusan 40," in ji Abubakar.
Irin yanayin da mazauna birnin Abuja ke ciki kenan babu na kwaryar birnin babu na kewaye.
End of Wanda aka fi karantawa
Wata kididdiga da kamfanin tsaro na Beacon Consulting ya fitar ta nuna an samu hare-haren 'yan bindiga guda shida a watan Janairun 2024, inda kuma aka yi garkuwa da akalla mutum 71 a Abujar da kewaye.
Kididdigar ta kuma nuna cewa a shekarar 2023 an samu hare-haren 'yan bindiga guda 50 inda kuma aka sace mutum 247, a babban birnin tarayyar.
Harwayau, kamfanin na Beacon Conculting ya ce an fi samun matsalar tsaron a kananan hukumomi guda hudu daga cikin guda shida.
"Yankin Bwari da Kuje da Kwali an fi samun matsalar satar jama'a domin karbar fansa", in Malam Kabiru Adamu, shugaban kamfanin.
Asalin hoton, Getty Images
Birnin Abuja dai ya yi iyaka da jihohi hudu masu fama da matsalar tsaro da suka hada da jihar Kaduna daga arewaci da jihar Naija daga yammaci sai kuma jihar Kogi da jihar Nassarawa daga kudanci.
Shugaban kamfanin Beacon Consulting, Malam Kabiru Adamu ya ce "wadannan 'yan bindiga na kwarorowa Abuja ne ta hanyar tsaunuka da suka hade da dazukan wadancan jihohin masu fama da matsalar tsaro kuma da alama ba mu ga wasu matakan da aka dauka ba domin dakile shigowarsu.
A baya-bayan nan mun ga yadda jami'an tsaro suka shiga dazukan da kan duwatsu domin yin abin da suka kira 'shara' to amma ba mu ga hakan ya rage yawaitar hare-hare ba", in ji Malam Kabiru.
Sai dai Group Captain Sadiq Garba mai ritaya wani mai sharhi kan harkar tsaro ya ce shi yana da ra'ayi na daban dangane da yadda batagarin ke shiga Abuja musamman ma cikin birnin.
"Ni a ra'ayina masu satar mutanen Abuja a cikin garin suke kuma idan suka saci mutanen a cikin garin suke boye su. Gazawar birnin ce ta janyo hakan saboda a manyan biranen duniya akwai na'urori da ke hana aikata laifuka".
Malam Kabiru Adamu da Group Captain Sadiq Mai ritaya sun ce abubuwa guda hudu ne suka ja hankalin 'yan bindiga suka rinka kwara zuwa Abuja.
Asalin hoton, Getty Images
Matsalar hare-hare dai na nuna irin gazawa na tsarin tsaron Najeriya kuma masana na ganin mafita ita ce komawa tsarin domin inganta shi.
"Shi tsarin tsaro yana amfani da Dan adam, kimiyya da tsari", in ji Kabiru Adamu.
Malam Kabiru Adamu ya ce akwai wasu tsare-tsare guda biyar da ya kamata jami'an tsaron birnin tarayyar su dabbaka kamar haka:
1- Damar hana bata-gari aiwatar da mugun aiki da ake kira da Turanci 'Deter'.
2- Daukar matakan da za su janyo wa mai son aikata laifi jinkiri da ake kira 'delay.
3- Agaji da za a kai wa wanda abin ya shafa wanda ake kira 'response' da turanci.
4- Bibiyar masu laifi bayan aikata laifi wanda zai bayar da damar kai wa ga kama mai laifi abin da ake kira 'tracing or tracking'.
5 – Yin waiwaye ga tsarin domin gyara inda aka samu matsala.
Daga karshe Malam Kabiru Adamu da Group Captain Sadiq Garba mai ritaya sun amince cewa dole ne jami'an tsaron Abuja da na jihohi masu makwabta su yi aiki tare sannan a yi aiki da fasaha kamar sanya kamarori masu daukar hoton masu laifi.
"Kari a nan shi ne ya kamata kuma a sanya al'umma da sarakunansu cikin al'amarin," in ji Malam Kabiru.
Masanan dai na da kwarin gwiwar cewa idan har aka aiwatar da wadannan shawarwari batun matsalar 'yan bindiga a babban birnin tarayya za zama sai dai wata matsal kuma ba ita ba.
Hakan kuma zai bai wa mazauna birnin irin su Abubakar Isa dan asalin Kano mazaunin Abuja kyakkayan fata na ci gaba da zama a birnin cikin aminci.
© 2025 BBC. BBC ba za ta dauki alhakin abubuwan da wasu shafukan daban suka wallafa ba. Karanta hanyoyin da muke bi dangane da adireshin waje.
Shin me ya sa Abuja ke fuskantar matsalar tsaro? – BBC
